top of page
  • Writer's pictureArtv News

NDLEA ta kama tsohon -soja ɗan shekara 90 da laifin kai wa ƴan ta’adda ƙwayoyi


Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi, NDLEA ta kama wani ɗan shekara 90, Usman Adamu a Mailalle, Sabon Birni a Sokoto da laifin kai wa ƴan fashin daji ƙwayoyi.


Kakakin hukumar, Femi Babafemi ne ya faɗi hakan a wata sanrwa da ya fitar jiya Lahadi a Abuja.


Babafemi ya ce an kama wanda a ke zargin ne tun 3 ga watan Agusta.


Ya ƙara da cewa an kama shi ne da kilo 5.1 na tabar wiwi.

37 views0 comments
bottom of page