Artv News
NAHCON ta yi nadama kan gazawarta wajen kwashe maniyyata aikin hajin bana

Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) cikin kaskantar da kai ta amince da abubuwan da suka faru: cewa tana da nadama mai mai yawa ga daukacin alhazan da suka shirya zuwa aikin Hajjin 2022 saboda wahalhalu da rashin jin dadi da suka samu a lokacin aikin jigilar jirage zuwa kasa mai tsarki.
A nasarawar da mataimakiyar daraktar hulda da jama'a ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, Hukumar ta makamancin wannan hakuri ga gwamnatin tarayyar Najeriya, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi, kamfanonin jigilar alhazai masu gudanar da yawon bude ido, da sauran jama’a kan duk wani abin ya faru a makonnin da suka gabata.
Abin takaicin shi ne, duk da kokarin da aka yi na jigilar dukkan maniyyatan Najeriya da ke son zuwa kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin 2022, NAHCON ta gaza wajen sauke wannan nauyi, musamman sakamakon koma bayan da aka samu a karshen makon da ya gabata da ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar maniyyatan zuwa ranar 27 ga watan Yuni na wannan shekara. Sai dai abin takaicin shi ne, zabin jirage da aka yi hayar da ya baiwa hukumar NAHCON da kuma masu gudanar da jigilar maniyyatan kamfanonin yawon bude ido masu zaman kansu su ma ya ci tura saboda asusunsu na IBAN ya gaza samun amincewar hukumomin Saudiyya.
Musamman, wadannan adadin maniyyatan da abin ya shafa ba za su je Saudiyya kafin rufe filin jirgin sama na Jeddah ba, don haka za su yi hajjin bana. Su ne: Mahajjata tara (9) daga jihar Bauchi; Alhazai 91 daga jihar Filato; Mahajjata 700 ne daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu yawon bude ido masu zaman kansu.
Hukumar ta ba da tabbacin cewa za a mayar wa dukkan maniyyatan da abin ya shafa kudin aikin Hajjinsu yayin da za ta yi kokarin gyara kuskuren da ta yi a nan gaba.
NAHCON ta koyi darussa da dama kuma ta kuduri aniyar kada a sake maimaita irin halin da ake ciki. shugabancin hukumar ya san cewa babu adadin uzuri da zai iya biya don takaicin da wasu muminai ke fuskanta a halin yanzu