top of page
  • Writer's pictureArtv News

Mun Gano Kayan Sojoji Da Tarin Kudade A Gidan Tukur Mamu – DSS


Hukumar Tsaro ta DSS ta ce ta kama kayayyakin da suka hada da kakin sojoji da kudaden kasashen waje da dama a gidan Tukur Mamu, dan jaridar nan da ke shiga tsakani da ’yan bindiga.


Kakakin hukumar ta DSS, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan lokacin da yake tsokaci a kan sakamakon binciken da suka yi a gidan mawallafin jaridar nan ta Desert Herald da sanyin safiyar Alhamis.


DSS ta kuma ce ta kama abubuwa da dama a gidan, kuma da zarar ta kammala bincike za ta maka shi a agaban kotu.


A cewar Afunanya, “Yanzu haka, jami’an tsaron sun samu izinin bincike gidansa da ofishinsa, kuma a nan ne aka sami irin wadannan kayayyakin.


“Sauran kayayyakin sun hada da kudaden kasashen waje daban-daban da abubuwan hada-hadar kudi.


“Yayin da muke ci gaba da bincike, tabbas za mu gurfanar da shi a gaban kuliya,” inji Kakakin na DSS.


A ranar Laraba ce dai hukumar ta cafke Tukur Mamu a filin jirgin sama na Kano, bayan ta sa an tiso mata keyarshi daga kasar Masar.

(AMINIYA)

635 views0 comments
bottom of page