top of page
  • Writer's pictureArtv News

Gwamna Ganduje zai rantsar da sababbin kwamishinoni a ranar Juma'a


Gwamnan jihar Kano, Dr.Abdullahi Umar Ganduje zai rantsar da sababbin kwamishinoni tara a ranar Juma’a 2 ga watan Satumba. Wadanda majalisar dokokin jihar ta tantance tare da amincewa da nada su, za su maye gurbin mambobin majalisar zartaswar jihar da suka yi murabus domin neman mukamai a zaben 2023 mai zuwa. Sanarwar da kwamishinan yada labarai Malam Muhammad Garba ya fitar ta nuna cewa an shirya gudanar da bikin rantsarwar ne a filin wasa na Sani Abacha Indoor da ke kofar Mata Kano da karfe 2:00 na rana. Gwamnan zai bayyana ma’aikatun su daga baya bayan rantsar dasu Wadanda za a rantsar sun hada da Malam Ibrahim Dan’Azumi Gwarzo, Alhaji Abdulhalim Abdullahi, Hon. Lamin Sani Zawiyya, Hon. Ya'u Abdullah , Hon Yusuf Abubakar. Sauran su ne Dr. Yusuf Jibrin Rurum Ali Musa Hamza da Adam Abdu Fanda Aminu Ibrahim Tsanyawa da Hon. Saleh Kausani da Alhaji Kabiru Mohammed

18 views0 comments
bottom of page