Artv News
APC ta bayyana Lalong a matsayin daraktan yakin neman zaben shugaban kasa

A ranar Alhamis din da ta gabata ne jam’iyyar (APC) ta gabatar da Gwamna Simon Lalong na jihar Filato kuma shugaban kungiyar gwamnonin Arewa a matsayin Darakta Janar na kungiyar yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar.
Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Sanata Abdullahi Adamu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a Abuja.
Shugaban na kasa ya jagoranci dan takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, da dan takarar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima zuwa wata ganawa da shugaban kasar a ofishin sa.
Hakazalika Adamu ya kaddamar da tsohon karamin ministan kwadago da samarwa Festus Keyamo a matsayin kakakin riko na kungiyar yakin neman zaben, yayin da mataimakiyar mai magana da yawunta Barr Hanatu Musa Musa.
A cewarsa, taron ya kasance domin yiwa shugaban kasa bayani da kuma samun amincewar sa kan tsare-tsare na jam’iyyar dangane da kayyakin yakin neman zabe da tsare-tsare kuma za a yi karin bayani nan ba da jimawa ba.