top of page
  • Writer's pictureArtv News

‘Abba Kyari Bai Tsere Daga Gidan Yarin Kuje Ba’


Hukumar Kula da Gidajen Gyaran Hali ta Najeriya (NCoS) ta ce dakataccen tsohon Mataimakin Kwamishinan ’Yan Sanda, DCP Abba Kyari bai tsere daga gidan yarin Kuje ba bayan harin da aka kai.


Abba Kyari, wanda ke fuskantar tuhume-tuhume kan zargin safarar miyagun kwayoyi, an aike da shi gidan yarin na Kuje.


A baya dai ana ta nuna fargabar cewa watakila Abban ya tsere daga gidan bayan wasu maharan sun farmaki gidan tare da sakin daruruwan fursunoni.


Aminiya ta rawaito yadda ’yan bindigar suka fada gidan sannan suka saki fursunonin, ciki har da wadanda ake zargi da kasancewa rikakkun ’yan Boko Haram.

37 views0 comments
bottom of page